Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar tsohon gwamnan Babban Bankin Najeria na zuwa neman maganin rashin lafiyar da ba a bayyana ba a ƙasashen waje
Emefiele, wanda kotu ta bayar da belinsa kan zargin almundahana, an kuma tuhume shi da laifuka da suka hada da buga sabbin kuɗi da fitar da biliyoyin naira ba tare da amincewar shugaban ƙasa ba.
A makon da ya gabata ne, Emefiele ya nemi kotu ta ba shi fasfo dinsa domin tafiya Birtaniya neman magani, lauan EFCC da ya shigar da ƙara ya ƙalubalanci buƙatar inda ya ce barin tsohon gwamnan Babban Bankin barin Najeriya hatsari ne.
EFCC ta shigar da sabbin tuhume-tuhume kan Emefiele, tana zarginsa da cin mutuncin ofishinsa da rashawa a lokacin da yana gwamnan Babban Bankin.