Kotu Ta Jingine Dokar Rushe Masarautun Kano

Spread the love

Wata babbar kotun tarayya da ke  Kano ta yi watsi da duk wani mataki da gwamnatin jihar  Kano ta dauka na soke dokar masarautar Kano.

Majalisar dokokin Kano ta soke dokar bayan haka Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aiwatar da ita ta hanyar tsige Alhaji Aminu Ado Bayero a matsayin Sarkin Kano.

Gwamnan ya kuma sauya salon kafa masarautu hudu da suka hada da Bichi da Rano Karaye da kuma Gaya da magajinsa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya yi.

An dogara da dokar ne ta sake nada Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II, wanda Ganduje ya tsige a shekarar 2020, a matsayin Sarkin Kano na 16.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *