Kotu ta rushe ƙananan hukumomi 33 da tsohon gwamnan Ondo ya ƙirƙiro

Spread the love

Babbar kotun jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya ta rushe kananan hukumomin mulki 33 da tsohon gwamnan jihar marigayi Oluwarotimi Akeredolu ya kirkiro.

A hukuncin da alkalin kotun, Justice A. O Adebusuoye ya yi a yau Alhamis ya bayyana Kananan hukumomin da cewa ba a kirkiro su bisa doka ba.

Alkalin ya zartar da cewa abu ne da ya saba wa doka, ga gwamna ya sanya hannu a kan wata doka a wajen jiharsa.

Kotun ta kara da cewa dokar da marigayi Akeredolu ya sanya wa hannu ta kirkiro kananan hukumomin a 2023 a Ibadan, babban birnin jihar Oyo, ta saba wa doka, a don haka ba ta da halarci.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, kamfanin dillancin labarai na Najeriya, wato NAN, ya ruwaito cewa a ranar 9 ga watan Satumba na 2023 Akeredolu ya sanya hannu a kan kudurin dokar kirkiro kananan hukumomi 33 a jihar, kudurin da kakakin majalisar dokokin jihar Chief Oladiji Olamide ya gabatar masa a gidan shi tsohon gwamnan da ke Ibadan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *