Kotu ta tura masu zanga-zangar #EndBadGovernance zuwa gidan yarin Kuje

Spread the love

Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta tura wasu daga cikin waɗanda suka gudanar da zanga-zangar tsananin rayuwa zuwa gidan yarin Kuje, bayan sun ƙi amsa tuhumar laifin cin amanar ƙasa.

A zaman kotun, mai shari’a Emeka Nwite ta bayar da umarnin a ajiye su har zuwa lokacin da za a saurari ƙara dangane da bayar da belin su a ranar 11 ga watan Satumba.

Mutanen da ake tuhumar dai sun musanta dukkan laifukan da Gwamnatin Tarayyar Najeriya ke tuhumar su da aikatawa guda shida da suka jiɓanci ta’addanci.

DANDALIN KANO FESTIVAL

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *