Kotu ta umarci Aminu Ado ya daina ayyana kansa a matsayin Sarkin Kano

Spread the love

Babar kotun jihar kano ta umarci sarkin Kano na 15, Mai martaba Aminu Ado bayero da ya daina kira ko gabatar da kansa a matsayin Sarkin Kano.

Haka kuma kotun ta bayar da umarni ga ƴansanda da su fitar da shi daga fadar Sarkin Kano da ke unguwar Nassarawa a cikin jihar.

A umarnin da kotun ta bayar bayan da ta karanta bukatar da lauyan gwamnatin jihar Kanon Ibrahim Isa Wangida ya gabatar mata, kotun ta zartar da umarnin na wucin-gadi.

Bayan Alhaji Aminu Ado Bayero, kotun ta kuma umarci sauran sarakuna hudu da aka rushe da su daina ayyana kansu a matsayin sarakunan masarautun.

Masarautun da aka rushe dai su ne wadda tsohuwar gwamnatin jihar kanon ta APC karkashin Dakta Abdullahi Umar Ganduje ta kirkiro wato Kano da Bichi da Gaya da Rano da kuma Karaye.

Wannan dai na zuwa ne bayan da Sarkin na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero ya gabatar da zaman fada a yau Litinin.

Babbar kotun ta dage zaman sauraren karar wadda aka shigar a gabanta ranar 24 ga watan nan na Mayu 2024, zuwa ranar 11 ga watan Yuni shekara ta 2024 domin saurare.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *