Kotun koli ta yi watsi da ƙarar da ke kalubalantar dokar kafa EFCC

Spread the love

Kotun kolin Najeriya ta ƙori ƙarar da wasu manyan alkalai na jihohi suka shigar, inda suke kalubalantar dokar da ta kafa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC.

Tawagar alkalai mai mambobi bakwai da alkali Uwani Abba Aji ta jagoranta, sun amince da ƙorar ƙarar saboda ba ta cancanci a saurare ta ba.

Ƙarar wadda alkalai na jihohi 16 suka shigar, na neman a rushe EFCC.

Yayin da wasu jihohi suka janye daga ƙarar, wasu sun ki yin haka inda suka ce za su kalubalanci lamarin.

Jihohin da suka shigar da ƙarar sun haɗa da Ondo da Edo da Oyo da Ogun da Nasarawa da Kebbi da Sokoto da Jigawa da Enugu da Benue da Anambra da Filato da Cross River da kuma Niger.

Sai dai a lokacin sauraron ƙarar ranar 22 ga watan Oktoba, jihohin Imo da Bauchi da kuma Osun su ma sun shiga cikin ƙarar yayin da Anambra da Ebonyi da kuma Adamawa suka sanar da janye wa daga ƙarar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *