Kotun ƙoli ta haramta ware guraben aiki ga keɓaɓɓun mutane a Bangaldesh

Spread the love

Kotun ƙoli a Bangaldesh ta yi soke mafi yawan sassan dokar da suka yi tanadin guraben aiki ga keɓaɓɓun mutane da ya janyo zanga-zanga a sassan ƙasar.

Tun a farkon wata dubban ɗalibai ke zanga-zanga a ƙasar domin nuna rashin amincewa da tsarin da ya ware ayyukan gwamnati ga wasu keɓaɓɓu da suke makusantan gwamnati ne.

Kotun ta bayar da umarnin keɓe kashi 93 na gurabn aiki a ƙasar domin bai wa duk wanda ya dace, yayin da ta ware kashi biyar ga iyalan ƴan mazan jiya da suka yi yaƙin ƙwatar ƴancin ƙasar na 1971.

Kotun ta kuma ware kashi biyu ga mutanen da suka fito daga ƙananan ƙabilu marasa rinjaye ko kuma masu buƙata ta musamman.

A baya dai ana ware kashi ɗaya cikin uku na guraben aikin yi a ƙasar ne ga iyalan ƴan mazan jiya.

Yanzu haka dai babu mutane a kan titunan birnin Dhaka, saboda dokar hana fita da gwamnati ta sanya bayan ɓarkewar zanga-zanga.

Mutane aƙalla 115 aka kashe tun bayan fara zanga-zangar amma wasu rahotanni na cewa adadin ya zarce haka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *