Ku tuba ko mu aika ku lahira – Matawalle ga masu ba ƴanbindiga bayanai

Spread the love

Ƙaramin ministan tsaro, Alhaji Bello Matawalle ya yi gargaɗi ga masu ba ƴanbindiga bayanai da su tuba, ko kuma su aika su lahira.

Matawalle ya yi wannan bayanin a ƙauyen Gundume da ke ƙaramar hukumar Sabon Birni da ke jihar Sokoto a lokacin da ya kai ziyarar aikin da sojojin ke yi a ranar Alhamis kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Ministan ya ce, “wannan ƙauyen a da cike yake da mutane, inda ake gudanar da hada-hada sosai. Ina tabbatar muku cewa za a samu zaman lafiya. Za mu kafa sansanin soji a nan.

“Amma kuma dole ku ji tsoron Allah. Masu ba ƴanbindiga bayanai a kan jami’an tsaro da zirga-zirgar mutane su daina. Ko dai ku daina, ko mu aika ku lahira,” in ji shi.

Tun farko kuma a ranar Laraba a wajen ƙaddamar da aikin soji na “Fansan Yamma”, ministan ya yi kira da a ba jami’an tsaro haɗin kai domin samar da zaman lafiya a yankin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *