Kwamitin zaman lafiya na Kano ya gargaɗi tubabbun yan daba

Spread the love

Kwamitin zaman lafiya na jihar kano ya ja hankali tare da gargadin tubabbun matasan yan daba game da tada hargitsi ko taba kayan Jama’a yayin zanga-zangar da ake gudanarwa yau Alhamis daya ga watan Augusta 2024, sakamakon tsadar rayuwa, fatara, da yunwa.

Shugaban sakatariyar kwamitin zaman lafiya na jihar Kano Ambasada Ibrahim Wayya, ne ya ja hankalin tare da nusar da matasan a taron da kwamitin yayi da tubabbun han daba da kuma yan jaridu a Kano.

Wayya ya jan hankalin tubabbun Matasan yan dabar tare da nusar dasu illar aikata barna ko hargitsi da razana alumma ne, a dakin taro na inganta tsaro da shiyasa dake Nasarawa GRA anan Kano.

Wayya ya ce shugabancin kwamitin ya ce ba zai shiga zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a fadin kasar nan ba, sakamakon rashin sanin Jagororin zanga-zangar.

Ya ce kwamitin ya tattauna da tubabbun yan dabar wanda su ka yi masa alkawarin ba za su bada gudunmawa ayi tashin hankali ko barnata dukiyar al’umma ba.

A jawabinsa daya daga cikin jagororin tubabbun yan dabar a Kano mai suna Kamilu Adakawa, ya yi Alkawarin cewa baza su taba tayar da hankalin ko su bada gudunmawa wajen yin wani hargitsi a fadin jihar nan ba.

Ya ce su da mabiyansu za su yi zanga-zangar lumana ne ta hanyar ayyanawa gwamnatin jihar Kano koken su, da kuma halin da wasu da dama a cikinsu suke ciki, na rashin aikinyi, rashin jari, da kuma masu bukatar a maidasu makaranta, wanda Shi ne silar fadawarsu halin da suke ciki.

Adakawa ya kara da cewa sun gamsu da yadda kwamitin zaman lafiyar na Kano ya bada damar kai kokensu ga gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf domin kaiwa ga shugaban kasa.

Taron wanda akayi da Matasan tubabbun yan dabar manya da kanana, ya sami halartar maitaimakawa gwamnan jihar Kano akan harkokin tsaro Aminu Muhammad Getso.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *