Mahaifiyar Gwamnan Jigawa Ta Rasu

Spread the love

 

Mahaifiyar Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, Hajiya Maryam Namadi Umar ta rasu.

 

Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da sakataren watsa labaran gwamnan, Hamisu Mohammed Gumel ya fitar, inda ya ce mahaifiyar gwamnan ta rasu ne a ranar Laraba, 25 ga Disamban 2024.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa za a jana’izarta ne da misalin ƙarfe 4:30 na yamma a Kafin Hausa.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *