Mai gida ya sallami ‘kiya-teka’ kan ƙara kuɗin haya

Spread the love

Wani mai gidan haya ya rage kuɗin haya tare da korar ‘kiya-tekan’ gidansa  saboda ƙara kuɗin haya ba da izininsa ba.

Mai gidan ya kori kiya-tekan ne bayan da ya gano cewa ya ƙara wa ’yan haya kuɗi a ɓoye kuma yana cinye kuɗin, a garin Asana, fadar Jihar Delta.

Daga nan ya zaftare wa ’yan hayan rabin kuɗin hayan da suke biya, wanda ’yan hayan suke kukan cewa ya yi tsada.

A baya wasunsu na biyan N600,000 a kan gida mai ɗakuna biyu da falo, masu ɗaki uku da falo kuma suna biyan N1,000,000.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *