Majalisar dattawa Najeriya ta amince kafa kwamitin kudi na CBN

Spread the love

Majalisar dattawan Najeriya ta tabbatar da nadin mutane 12 karkashin jagorancin gwamnan babban bankin kasar, Olayemi Cardoso,a matsayin mambobin kwamitin da za su kula da harkokin kudi a babban bankin Kasar CBN.

Wannan tabbacin ya zo ne bayan wani rahoton kwamitin kula da harkokin banki da inshora da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi na babban bankin ya gabatar a zaman majalisar da aka yi ranar Alhamis.

Tabbatar da sabbin mambobin MPC ɗin na zuwa ne kwanaki kaɗan kafin taron tsare-tsaren babban bankin na farko karkashin sabon gwamnan bankin.

An tsara taron ne a ranakun 26 da 27 ga Fabrairu, 2024.

Membobin su ne:

1. Olayemi Cardoso – Shugaba

2. Muhammad Sani Abdullahi – Mamba

3. Bala M. Bello – Mamba

4. Emem Usoro – Mamba

5. Philip Ikeazor – Mamba

6. Lamido Yuguda – Mamba

7.Jafiya Lydia Shehu – Mamba

8. Murtala Sabo Sagagi – Mamba

Ba mu da labarin buhun siminti ya kai 15,000 a Kasuwa : Fatima Dangote

Gwamnati za ta ƙara yawan mutanen da za ta bai wa tallafin kuɗi

9. Aloysius Uche Ordu – Mamba

10. Aku Pauline Odinkemelu – Mamba

11. Mustapha Akinwumi – Mamba

12. Bandele A.G. Amoo – Mamba

A watan Nuwambar 2023, Cardoso, wanda shugaba Tinubu ya naɗa a matsayin gwamnan CBN a watan Satumba na 2023, ya ce taron na MPC bai yi tasiri ba a karkashin magabacinsa Godwin Emefiele.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *