Majalisar dattawa ta amince Tinubu ya ciyo bashin naira triliyan 1.77

Spread the love

Majalisar dattawa ta Najeriya ta amince da buƙatar shugaban ƙasa Bola Tinubu na ciyo bashin $2.2, wanda ya kai kimanin naira triliyan 1.77.

Majalisar ta amince da buƙatar ne bayan kwamitin ciyo bashi daga ciki da wajen ƙasar, ƙarƙashin jagorancin Sanata Aliyu Wamakko wai wakiltar Sokoto ta arewa ya gabatar da rahotonsa.

Daily Trust ta ruwaito cewa idan aka karɓo wannan sabon bashin, bashin ake bin Najeriya zai kama naira triliyan 136 ke nan.

Tinubu ya aika wa majalisar buƙatar ciyo bashin ne, wanda ya ce zai yi amfani da shi domin cike giɓin kasafin kuɗin bana na.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *