Majalisar dokokin Kano ta miƙa wa gwamna sabuwar dokar masarautu

Spread the love

Kakakin majalisar dokokin jihar Kano, Jibril Falgore tare da rakiyar wasu jagororin majalisar sun isa gidan gwamnati domin kai wa gwamna sabuwar dokar masarautu da majalisar ta yi wa kwaskwarima.

Dazu da safe ne majalisar ta yi wa dokar masarautun jihar ta shekara 2019 kwaskwarima, inda ta soke duka masarautun jihar biyar.

Wakilin BBC da ke Kano ya ce a halin da ake ciki gwamnan tare da ‘yan majalisar suna cin abincin rana ne a gidan gwamnati, inda ake sa ran gwamnan zai saka hannu kan sabuwar dokar da zarar sun kammala cin abincin.

Wasu majiyoyi a gidan gwamnatin sun shaida wa wakilin namu cewa tuni masu zaɓen sarki a Kano suka isa fadar gwamnatin jihar, wataƙila domin shirye-shiryen zaɓen sabon sarki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *