Majalisar wakilan Najeriya ta tabbatar da naɗin Laftanar Janar Olufemi Oluyede a matsayin babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya.
Hakan na zuwa ne bayan gabatar da rahoton kwaitin da aka kafa domin tantance shi ranar Laraba.
Tun da farko, shugaba Bola Tinubu ya naɗa Janar Oluyede a matsayin muƙaddashin babban hafsan sojin ƙasa bayan mutuwar Laftanar Janar Taoreed Lagbaja.
Shugaban kwamitin da ya tantance shi, Babajimi Benson, wanda ya gabatar da rahoton, ya ce an yi wa Oluyede tambayoyi kan batutuwan tsaro na ƙasa kuma ya amsa su yadda ya kamata.
Ya ce kwamitin ya gamsu da kwarewarsa kuma saboda haka zai iya rike ofishin da aka ba shi.