Malala Yousafzai za ta ziyarci Pakistan karon farko cikin shekaru

Spread the love

Fitacciyar ‘yar gwagwarmayar Ilimi kuma wadda ta taɓa lashe kyautar Nobel, Malala Yousafzai, ‘yar asalin Pakistan, za ta ziyarci ƙasarta ta haihuwa a karon farko cikin shekaru.

Matashiyar mai shekara 27 za ta halarci wani taro na kwana biyu – da zai mayar da hankali kan ilimin yara mata a ƙasashen musulmi.

An fitar da Malala Yousafzai daga Pakistan a shekarar 2012 bayan da wani ɗan ƙasar na ƙungiyar Taliban ya harbe ta a ka lokacin da take cikin motar ɗaukar ɗalibai.

Tun daga lokacin sau ƙalilan ta ziyarci ƙasar.

An gayyaci shugabannin Afghanistan waɗanda ‘yan Taliban ne – da ke taƙaita wa mata neman ilimi – zuwa taron, kodayake ba su ce komai ba game da gayyatar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *