Matsalar Ƙofa Ta Hana Fasinjoji 58 Hawa Jirgin Abuja Zuwa Landan

Spread the love

Kamfanin jirgin sama na British Airways ya hana fasinjoji 58 hawa jirginsa da zai tashi daga Abuja zuwa Landan saboda matsala da ƙofar jirgin ta samu.

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA), ta ce kamfanin jirgin ya bar wasu kujeru babu kowa saboda dalilan tsaro.

Daraktan Yaɗa Labarai da Kare Haƙƙin Fasinjoji na NCAA, Mista Michael Achimugu, ya wallafa a shafinsa na X cewa matsala ce ta sa aka hana fasinjojin hawa jirgin.

Ya ce an bai wa fasinjoji 30 wajen kwana a wani otel, yayin da 28 suka koma gidajensu.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *