Kocin Bayern Munich Thomas Tuchel ya ce gasar ɗaukar Bundesliga ta ƙare bayan rashin nasarar da ya yi da ci biyu babu ko daya a hannun Borussia Dortmund, duk da cewa a kwai wasa bakwai da ya yi ragowa a kakar.
Kwallayen da Dortmund ta ci sun fito ta hannun Karim Adeyemi da Julian Ryerson, nasarar farko da ta samu kan Munich a wasan hamayya na Der Klassiker tun 2019.
Da wannan rashin nasara, yanzu maki 13 ne tsakanin Leverkusen da ke ta ɗaya da Bayern da ke matsai na biyu.
- Kocin Manchester United Ya Ce Bai Damu Da Jita-jitar Da Ake Yaɗawa Ba .
- Yansanda sun kama wani malami da sassan jikin ɗan adam a Najeriya
Ko da aka tambaye shi ko Bayern ta hakura da wannan kofin, sai Tuchel ya ce “eh ko shakka babu.”
A makon jiya ne kocin Leverkusen Xavi Alonso ya bayar da tabbacin ci gaba da zama a ƙungiyar, wanda hakan ya kawo ƙarshen jita-jitan da ake yi na maye Jurgen Klopp a tsahuwar kungiyarsa Liverpool.