Najeriya Ta Doke Ghana A Wasan Sada Zumunta

Spread the love

Tawagar Super Eagles ta Najeriya ta doke takwararta Black Stars ta Ghana a wani wasan sada zumunta da suka fafata yau Juma’a a kasar Morocco.

An dai tashin wasan ne 2–1, inda Najeriya ta yi galaba a kan makwabciyarta da ke Yammacin Afirka.

Dan wasan Najeriya Cyriel Dessers ne ya ci kwallon farko a bugun fenariti a minti na 38, sannan a minti na 84 kuma Ademola Lookman ya zura tasa kwallon.

Ghana ta ci kwallonta ne da bugun fenariti ta hannun dan wasanta Jordan Ayewa gab da ana kusan tashi a wasan.

Daya daga cikin ’yan wasan bayan Ghana ya Jerome Opoku ya samu jan kati a minti na 56 da soma wasan.

Haduwar kasashen biyu na zuwa ne kasa da watanni biyu bayan kammala Gasar Kofin Nahiyyar Afirka na AFCON da aka yi a Ivory Coast wacce ta lashe kofin.

Najeriya ta kai wasan karshe a gasar yayin da aka cire Ghana tun a zagayen rukuni-rukuni, lamarin da ya yi sanadin korar mai horar da ‘yan wasan kasar.

 

Shugaban Jami’ar MAAUN Farfesa Gwarzo, Ya Bayar Da Kyautar Motocin Aiki 2 Ga Ofishin Yan Sandan Hotoro Kano.

ya nuna sau 56 Najeriya da Ghana suka kara a fagen kwallon kafa a gasa daban-daban da wasannin sada zumunci.

Kazalika, Taiwo Awoniyi da Tyronne Ebeuhi da Gabriel Osho duk ba su samu halartar wasan na sada zumunci ba.

A bangaren Ghana, fitaccen dan wasan kasar Thomas Partey, shi ma bai samu zuwa wasan ba.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *