NATO ta ƙaddamar da atisayen soji don daƙile samamen Rasha

Spread the love

Kungiyar tsaro ta NATO ta ƙaddamar da atisayin soji mafi girma tun bayan yaƙin cacar-baka, inda ta tura dubban dakaru don daƙile duk wani yunƙurin samame daga Rasha.

Ƙungiyar ta ce hakan zai nuna haɗin kai, da kuma ƙarfin da take da shi.

Wannan na zuwa ne yayin da ake hasashen cewa Donald Trump zai iya lashe zaɓen shugaban ƙasar Amurka, kuma a baya ya sha alwashin cewa Amurka ba za ta kai wa Turai ɗauki ba, idan Rasha ta kai mata hari.

An ƙaddamar da atisayin ne a Virginia, inda aka sallami dakarun Amurka da jiragen ruwanta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *