Najeriya ta tura dakaru na musamman Gwoza na musamman Gwoza

Spread the love

Rundunar ‘yansandan Najeriya ta tura ƙarin dakaru na musamman yankin ƙaramar hukumar Gwoza na jihar Borno domin tsaurara tsaro bayan harin bama-bamai da ya kashe mutum 18 ranar Lahadi.

Da yake miƙa ta’aziyyarsa ga al’ummar jihar a yau Litinin, Sufeto Janar na ‘Yansadan Najeriya IGP Kayode Adeolu Egbetokun ya ba da umarnin tura ƙwararrun dakarun rundunar a ɓangaren bama-bamai.

“Sashen abubuwan fashewa (EOD) na rundunar tare da haɗin gwiwar sojojin Najeriya na cigaba da aikin dudduba wurin don tabbatar da cewa babu sauran barazana,” a cewar wata sanarwa da kakakin runundar Olumuyiwa Adejobi ya fitar.

Lamarin ya faru ne lokacin da wasu ‘yan ƙunar bakin wake suka tayar da bama-baman da ke jikinsu a cikin mahalarta wani taron biki a ƙaramar hukumar Gwoza.

Gwamnatin jihar ta ce maharan sun yi amfani da “girman jihar ne da kuma ƙarancin tsaro a kan iyakoki” kafin su kai harin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *