Ramaphosa ba zai sauka daga muƙaminsa ba – jam’iyyar ANC

Spread the love

Mataimakiyar babban sakataren jam’iyyar ANC Nomvula Mokonyane ta sanar wa manema labarai a cibiyar kirga kuri’un zaɓen da aka gudanar a Afrika ta kudu cewa shugaba Cyril Ramaphosa ba zai sauka daga mukaminsa a matsayin shugaban jam’iyyar ba duk da rashin kyakkyawan sakamakon zaɓen da jam’iyyar ta samu.

Da aka tambaye ta game da yuwuwar tattaunawar hadin gwiwa, Mokonyane ta bayyana cewa, a halin yanzu, jam’iyyar ba ta shiga tattaunawa da wasu jam’iyyu ko ƙungiyoyi ba.

Ta kuma bayyana cewa a yau ne shugabannin jam’iyyar ANC za su yi taro domin tattauna sakamakon zaben da ake yi a yanzu.

An shirya gudanar da taron manema labarai da yammacin ranar Asabar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *