Rashin Tabbas Kan Aikin Haƙar Fetur Na Damun Mutanen Bauchi Da Gombe

Spread the love

Al’ummomin jihohi Bauchi da Gombe da kuma na Arewa sun fara nuna damuwa kan rashin tabbas game da aikin hako man fetur da aka kaddamar a jihohin biyu lokacin Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.

An faro wannan aiki ne tun a shekarun 1990 lokacin da aka fara ba da lasisin nemo man a rijiyoyi masu lamba (OPLs) 809 da 810 ga kamfanonin Shell da Chevron.

A lokacin an bukaci kamfanonin sun binciko man da ake hasashen samu, tare da hako rijiyoyin.

Kamfanin Shell ya hako rijiyar Kolmani-1 a kan OPL 809 sai Chevron ya hako Nasara-1 a kan OPL 810.

Kamfanonin biyu sun ba da rahoton gano iskar gas da za ta isa a yi kasuwanci kuma suka ce ba su samu man fetur mai yawa ba.

Daga nan sai Kamfanin Mai na Kasa (NNPC), ya ci gaba da aikin a shekarar 2019 ya ba da sanarwar gano danyen mai da iskar gas mai yawa.

Wannan albishir da kamfanin ya yi ya sa farin ciki ga ’yan Nijeriya, musamman mutanen Arewa.

Kamfanin NNPC ya ce, ya gano danyen man a rijiyar Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe, inda ya ce a rijiyar Kolmani akwai danyen man fetur fiye da ganga biliyan daya da gas da ya kai ganga biliyan 500.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *