Rundunar Yan Sandan Kano Ta Tabbatar Da Rasuwar Jami’an Ta 5 Wasu 10 Suka Jikkata.

Spread the love
SP Abdullahi Haruna Kiyawa Kakakin Yan sandan Kano

Rundunar yan sandan jahar Kano, ta tabbatar da rasuwar jami’an ta guda 5 , ya yin da wasu 10 suka samu raunuka a wani mummuna da ya rutsa  da su, a yankin karamar hukumar Kura  dake jahar.

Kakakin rundunar yan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ( Bawahala) ne ya bayyana hakan ga jaridar idongari.ng, a ranar Talata.

SP Abdullahi Kiyawa, ya ce a daren jiya suka samu rahotan faruwar hadarin a lokacin da jami’an yan sandan, suka dawo daga aikin da aka tura su , jahar Edo, inda wata Tirela ta ke yin ribas ba tare da sanya wata alama ba.

Idongari.ng, ta ruwaito cewa rundunar ta nuna alhini tare da  mika sakon ta’aziyarta ga iyalan wadanda suka rasu, da kuma yi mu su  addu’ar samun lafiya ga wadanda suka samu raunuka.

Itama hukumar kiyaye hadura ta kasa reshen jahar Kano, CRC Abdullahi Labaran, a madadin kwamandan hukumar Tijjani Mohammed, ya bayyana alhini da jimami, inda ya mika sakon ta’aziyarsa ga rundunar yan sandan jahar Kano da kuma iyalan wandand iftila’in ya faru da su.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *