Sai Al’umma Sun Tallafawa Mazauna Gidan Gyaran Hali : Hajiya Azumi Namadi Bebeji

Spread the love

 

Shugabar kwamitin yiwa daurarru afuwa a jihar Kano dake arewacin Najeriya Hajiya Azumi Namadi Bebeji, ta shawarci al’umma da su dinga taimakawa daurarrun dake gidan gyaran halin jihar.

Hajiya Azumi ta bayyana hakan ne a yayin zantawar ta da manema labarai a Kano, albarkacin karatowar karshen shekarar 2024 da muke bankwana da ita.

Ta kuma kara da cewa gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf na sane da daurarrun, kasancewar akwai tanade-tanade da ya ke yi musu a kowanne yanayi da ake ciki.

 

Haka kuma ta yabawa gwamnan da mataimakin sa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, a bisa yadda su ke gabatar da ayyukan alheri ga al’ummar jihar na birni da karkara.

 

A karshe ta yi fatan al’umma zasu dauki shawarar da ta basu, domin ya zama an dada sanya walwala a zukatan mazauna gidajen gyaran halin dake fadin jihar Kano.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *