Sai da aka sace ni na fara goyon bayan biyan kuɗin fansa : Tsohon daraktan DSS

Spread the love

Tsohon Daraktan Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), Mista Mike Ejiofor, ya bayyana cewa, tunaninsa na ƙin biyan kuɗin fansa na garkuwa da mutane ya canja bayan da a ka sace shi da kansa.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa ya yi watsi da batun biyan kuɗin fansa, ya jaddada cewa taɓarɓarewar tattalin arzikin da ake fama da shi a ƙasar nan na sa mutane shiga harkar garkuwa da mutane a matsayin wata hanyar samun kuɗin shiga.

Ejiofor ya amince da damuwar da ake samu game da ƙaruwar satar mutane tare da jaddada buƙatar samar da hanyoyin da za a bi don magance matsalar.

Abu shida da za ku yi don kauce wa bugun zuciya a lokacin kallon wasan ƙarshe a gasar Afcon

Ya ba da shawarar cewa ba lallai a kau da matsalar bakiɗaya ba, amma tana buqatar a tura isassun kayan aiki, tare da mai da hankali kan sa ido sosai don tabbatar da an yi amfani da kuɗaɗen da aka ware domin tsaro yadda ya kamata.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *