Tsohon Daraktan Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), Mista Mike Ejiofor, ya bayyana cewa, tunaninsa na ƙin biyan kuɗin fansa na garkuwa da mutane ya canja bayan da a ka sace shi da kansa.
Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa ya yi watsi da batun biyan kuɗin fansa, ya jaddada cewa taɓarɓarewar tattalin arzikin da ake fama da shi a ƙasar nan na sa mutane shiga harkar garkuwa da mutane a matsayin wata hanyar samun kuɗin shiga.
Ejiofor ya amince da damuwar da ake samu game da ƙaruwar satar mutane tare da jaddada buƙatar samar da hanyoyin da za a bi don magance matsalar.
Abu shida da za ku yi don kauce wa bugun zuciya a lokacin kallon wasan ƙarshe a gasar Afcon
Ya ba da shawarar cewa ba lallai a kau da matsalar bakiɗaya ba, amma tana buqatar a tura isassun kayan aiki, tare da mai da hankali kan sa ido sosai don tabbatar da an yi amfani da kuɗaɗen da aka ware domin tsaro yadda ya kamata.