Saudiyya na dab da samun damar karɓar baƙuncin gasar cin Kofin Duniya na 2034

Spread the love

Da alama za a tabbatar wa ƙasar Saudiyya damar karɓar baƙuncin gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa ta Duniya ta 2034, bayan FIFA ta amince da ƙoƙarinta wajen kare hakkin ɗan’adam a wani sabon rahoton tantance matsayinta kan kare haƙƙin bil-adama.

Hukumar ƙwallon ƙafa da Duniya FIFA ta bai wa ƙasar maki 4.198 cikin maki biyar – maki mafi yawa da aka bai wa ƙasashen da suka karɓi baƙuncin gasar Kofin Duniya a baya.

Duk da fargabar da ake da ita kan tarihin taƙe haƙƙin ɗan’adam a ƙasar, rahoton ya ce babu wata fargaba game da ‘yancin ɗan’adam a ƙasar.

Rahoton ya kuma ce gasar ka iya zama wani mataki na kawo sauye-sauye a fannin taƙe haƙƙin binl-adama a ƙasar.

Saudiyya ta kasance ƙasa ɗaya tilo da ke neman damar karɓar baƙuncin gasar cin kofin duniya ta 2034 bayan janyewar Australia a shekarar da ta gabata.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *