SERAP ta ce jami’an DSS sun yi wa ofishinta ƙawanya

Spread the love

Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya DSS) sun kai samame ofishin ƙungiyar SERAP, mai fafutikar yaƙi da cin hanci da Rashawa a Abuja.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta wallafa a shafinta na X, ta bayyana cewa jami’an tsaron sun yi wa ofishinsu ƙawanya ba bisa ka’ida ba, tare da neman ganawa da manyan daraktocin ƙungiyar.

Ƙungiyar ta yi kira ga shugaban ƙasar, Bola Tinubu da ya shiga tsakani, sannan ya umarci jami’an su daina abin da ƙungiyar ta kira ”tsangwama da cin zarafi, da kuma take haƙƙin ‘yan Najeriya”.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *