Shari’ar Murja Kunya: Hukumar Hisbah a Kano ta musanta labarin da ake yada wa kan murabus din kwamandan ta Sheik Aminu Ibrahim Daurawa

Spread the love

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta sanar da cewa har yanzu Babban Kwamnadanta, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa na nan kan kujerarsa bai yi murabus ba.

Mataimakin Babban Kwamandan Hisbah na Jihar, Sheikh Mujahid Aminuddeen Abubakar ne ya sanar da hakan.

Sheikh Mujahid ya bayyana haka ne bayan rade-radin da ke yawo cewa Sheikh Daurawa ya yi murabus, kan takaddamar sakin jarumar tiktok, Murja Ibrahim Kunya, daga gidan yari, bayan kotun Musulunci a ba da umarnin tsare ta.

A ranar Lahadi Aminiya ta ruwaito cewa an fitar da Murja daga gidan yari, sabanin umarnin kotu, lamarin da ya haifar da damua a cikin al’umma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *