Shugaban Senegal mafi ƙarancin shekaru ya sha rantsuwar kama aiki

Spread the love

Bassirou Diomaye Faye, ya sha rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban Senegal na biyar.

An rantsar da shi ne a Dakar, babban birnin ƙasar.

A watan da ya gabata ne, Faye mai shekara 44 ya lashe zaɓ da kashi 54 cikin 100 na ƙuri’un da aka jefa inda ya zarce abokin hamayyarsa Amadou Ba.

A ranar Juma’a ne majalisar tsarin mulkin ƙasar ta tabbatar da Faye a matsayin wanda ya ci zaɓe.

Shugabannin ƙasashe daga nahiyar Afirka sun halarci bikin rantsar da shi har da shugaban Najeriya Bola Tinubu wanda shi ne shugaban ƙungiyar Ecowas.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *