Shugabannin ƙwadago sun isa fadar shugaban ƙasa don ganawa da Tinubu

Spread the love

Shugabanin gamayyar ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya sun isa fadar gwamnatin ƙasar, domin ganawa da shugaban ƙasar Bola Tinubu.

Shugaban ƙasar ne dai ya gayyaci jagororin gamayyar ƙungiyoyar ƙwadagon zuwa fadarsa domin tattaunawa kan batun mafi ƙanƙantar albashi da aka kasa cimma matsaya akai.

Ƙungiyoyin ƙwadagon da gwamnatin Najeriya dai sun jima suna kai ruwa rana kan mafi ƙanƙantar albashin ma’aikata a ƙasar.

Tun da farko dai gwamnatin Najeriya ta yi wa kungiyar ƙwadagon tayin naira 62,000 a matsayin mafi ƙanƙantar albashi, yayin da kungiyoyi ƙwadago suka ce suna buƙatar gwamnati ta biya naira 250,000.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *