Rundunar Sojin Najeriya ta ce ta kashe wani jagoran ‘yan fashin daji a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin ƙasar.
Wata sanarwa da ta fitar a shafukanta na intanet ta ce dakarun rundunar da aka tura don yaƙi da ta’addanci ne suka yi nasarar kashe jagoran, wanda ba ta bayyana sunansa ba, a ranar Laraba.
“Bayan samun bayanan sirri, dakaru sun yi wa gungun ‘yanta’addan kwanton-ɓauna a wata mashiga da ke ƙauyen Sarma a ƙaramar hukumar Tangaza, inda suka yi nasarar kashe jagoransu tare da ƙwato bindigar AK-47 da kuma babur,” in ji sanarwar.
A jihar Kaduna kuma, dakarun sojin sun yi nasarar katse hanzarin masu garkuwa da mutane a garin Kafanchan na ƙaramar hukumar Jema’a, sannan suka kama biyu daga cikinsu tare da ƙwato bindiga ɗaya, da harsasai, da kuma babur.
Kazalika, wani ɗan fashi ya gamu da ajalinsa a wurin duba ababen hawa na Kaskara da ke ƙaramar hukumar Barikin Ladi ta jihar Filato, lokacin da dakarun suka amsa kiran neman agaji game da gungun ‘yanfashi a yankin.
- Fursunoni 118 sun tsere daga gidan yarin Suleja
- Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi Da Yin Amfani Da Ankwa Suna Kwacen Wayoyi A Adaidaita Sahu A Kano.