Sojojin Najeriya sun ce sun kashe ‘yan bindiga 11 a Katsina da Zamfara

Spread the love

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarun da ta tura don aikin murƙushe ‘yan ta-da-ƙayar-baya a jihohin Katsina da Zamfara sun yi nasarar kashe ‘yan bindiga 11 a cikin kwana biyu.

Sun dai kai samame ne maɓoyar waɗanda suka kira ‘yan ta’adda, inda suka kashe wani adadi na ‘yan bindigar a ranar 29 ga watan Maris.

Ta ce dakarun soji sun yi nasarar kai wa mafakar wani riƙaƙƙen ɗan fashin daji mai suna Hassan ‘Yan tagwaye hari, a cikin ƙaramar hukumar Tsafe, inda suka kashe uku a cikinsu tare da ƙwato makamai.

Rundunar sojin ta kuma ce dakarunta sun ragargaza sansanonin ɗan fashin, wanda ta ce yana da hannu wajen satar mutane da ayyukan ta’addanci a wasu yankuna na arewa maso yamma.

A jihar Katsina kuma, cewar rundunar sojin ƙasan Najeriya, dakarunta sun gwabza faɗa a ranar 30 ga watan Maris da waɗanda suka kira ‘yan ta’adda a Shawu Kuka da Shinda da Tafki da Gidan Surajo da Citakushi da Kabai I da Kabai II duka a cikin ƙaramar hukumar Faskari.

Ta ce dakarun sun yi nasarar kashe ‘’yan ta’adda’ takwas tare da gano bindigogi ƙirar gida guda uku da kakin sojoji da kuma ɗumbin hatsin sata.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *