Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan bindiga uku a dajin Sambisa

Spread the love

Rundunar sojin Najeriya da ke aikin yaƙi da ‘yan bindiga a yankin arewa maso gabashin Najeriya ta ce ta kashe ‘yan bindiga uku tare da lalata sansanin ‘yan bindigar a dajin Sambisa.

Cikin wata sanarwar da daraktan yaɗa labaran rundunar sojin ƙasa na Najeriya Onyema Nwachuku ya fitar, ya ce cikin waɗanda sojoin suka kashe har da ɗan ƙunar-baƙin-wake, tare da ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 biyu.

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa a wani samamen na daban da sojojin suka kai sansanin ‘yan bindigar – da ke yankin Buluwa na ƙaramar hukumar Kukawa – sun kashe wani ɗan bingida guda tare da ƙwato bindiga guda ƙirar AK-47 da harsasai 14 da babur guda ɗaya da kayan abinci da sauran kayayyaki.

Tinubu ya umarci Kwastam ta mayar da kayan abincin da ta kwace wa mutane

WOFAN HAS DISTRIBUTED BAND BICYCLES TO PEOPLE WITH DISABILITY TO MARK WOMEN INTERNATIONAL DAY

A baya-bayan dai matsalar tsaro na ci gaba da addabar wasu sassan arewacin Najeriya, inda a karhsne makon da ya gabata wasu da ake kyautata zato mayaƙan Boko Haram ne suka sace wasu ‘yan gudun hijira fiye da 100 a jihar Borno.

Haka ma a ranar Alhamis ɗin da ta gabata wasu ‘yan bindiga suka sace daliban makarantar furamare da na ƙaramar sakandiren Kuriga a jihar Kaduna.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *