Tchiani Ya Zargi Najeriya, Faransa, China Da Amurka Wajen Cutar Da Nijar

Spread the love

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya da haɗa baki da Faransa da China da Amurka wajen ɗaukar nauyin ayyukan ta’addanci a ƙasarsa.

A cikin wani jawabi na awa uku da aka watsa kai tsaye a gidan talabijin na Radio-Télévision du Niger (RTN) a ƙarshen mako, Tchiani ya yi magana da harshen Hausa, Zabarma da Faransanci, inda ya zargi Najeriya da Jamhuriyar Benin da Faransa da China da Aljeriya da Amurka da kokarin dagula ko cutar Nijar da sauran ƙasashen da ke cikin ƙawancen AES.

Wannan shi ne karo na biyu da Tchiani ke zargin Najeriya a yayin wata hira da ya yi ta ranar Kirsimeti a bara, inda ya ce Faransa na haɗa baki da ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya a yankin tafkin Chadi domin lalata tsaron Nijar, tare da sanin Najeriya.

Tchiani ya ƙara da cewa an gudanar da wata ganawa a ɓoye a Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya a watan Disamba na shekarar 2024 domin tsara yadda za a afka wa Nijar.

Haka zalika, Tchiani ya ce a watan Janairu 2025, wakilan Benin da Côte d’Ivoire da wasu ƙasashen Yammacin Afirka sun sake haɗuwa a Abuja domin sake nazarin dabarunsu na cutar da Nijar, amma suka gamu da cikas bayan shirin ya ci tura.

Waɗannan zarge-zargen sun biyo bayan hare-haren da ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya suka kai a yankunan Tahoua da Dosso, inda aka kashe sama da sojoji 100, lamarin da ya tayar da hankalin jama’ar Nijar.

Tuni gwamnatin Najeriya ta mayar da martani dangane da wannan sabon zargi, inda ta karyata iƙirarin gaba daya tare da bayyana shi a matsayin maras tushe ko makama.

Masu fashin baƙi dai na alaƙanta irin waɗannan zarge-zarge da shugaban sojin ya yi da ƙoƙarin wanke kansa da kuma burge al’ummarsa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *