Tinubu Ya Ba Wa Firaministan India Lambar Yabo

Spread the love

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karrama firaministan Indiya, Narendra Modi da lambar yabo ta biyu mafi daraja a ƙasar wato GCON.

Tinubu ya bayyana hakan ne a lokacin ganawa da Mista Modi a fadar gwamnatinsa da ke Villa a Abuja.

A ranar Asabar da daddare ne firaministan na Indiya ya isa Najeriya a wata ziyara ta kwana guda da zai yi a ƙasar

Shugaban na Najeriya ya ce ya bai wa Modi lambar girmamawar ce domin ”nuna godiyarmu ga Indiya a matsayin ƙawar Najeriya”.

Ziyarar Modin ita ce ta farko da wani firaministan Indiya ya kai wa Najeriya tun 2007, lokacin da Firaminitan na wancan lokaci Dakta Dr Manmohan Singh ya kai ƙasar.

Shugabannin biyu za su mayar da hankali a tattaunawrsu wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *