Tinubu Ya Nada Sabbin Shugabannin Hukumomin NIA Da DSS

Spread the love

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sauke shugaban hukumar ‘yansandan farin kaya ta DSS, Yusuf Bichi, tare da maye gurbinsa da Adeola Oluwatosin Ajayi a matsayin shugaban hukumar.

Kazalika, shugaban ya naɗa Mohammed Mohammed a matsayin shugaban Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa (NIA) domin ya maye gurbin Ahmad Rufai Abubakar, wanda ya ajiye aikinsa a ƙarshen mako.

Wata sanarwa da kakakin fadar shugaban ƙasa, Ajuri Nglale, ya fitar ta ce Mohammed ya fara aiki da NIA tun 1995 kuma ya yi karatu a Jami’ar Bayero da ke Kano.

Mista Adeola kuma shi ne mataimakin shugaban hukumar kafin naɗin nasa a yanzu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *