Tura ta kai bango —Masu zanga-zanga

Spread the love

Masu zanga-zangar tsadar rayuwa a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, sun ce, “tura ce ta kai bango, suka fito kan tituna.

“Za mu ci gaba da fitowa yin irin wannan zanga-zangar lumana har zuwa ranar 10 ga watan Agusta da muke ciki.”

Aminiya ta gano cewa kungiyoyin matasa daban-daban ne suka jagoranci zanga-zangar da suka zagaya sassan birnin Ibadan dauke da rubutattun kwalaye damke bayani a kan bukatar mahukunta su hanzarta daukar matakin kawo karshen matsalolin da miliyoyin jama’ar kasa suka fada ciki.

Masu zanga-zangar da suka samu rakiyar jami’an tsaro sun yi tattaki ne daga harabar Jami’ar Ibadan (UI) da kan hanyar Kasuwar Bodija da Zango da Mokola Round About da Iwo Road da Challenge da Apara da sauran fitattun unguwanni a birnin Ibadan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *