Wata kotu a Kano ta umarci yan kasuwar magani ta Sabongari su tashi su koma Dangoro

Spread the love

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta umurci dillalan magunguna dake kasuwar kasuwar Sabon Gari dake yankin Karamar Hukumar Fagge a Kano da su tashi nan take.

Baya ga haka, kotun ta kuma ba da umarnin mayar da masu sana’ar ta hada-hadar magunguna zuwa cibiyar da aka kebe don siyar da magunguna a Dangoro da ke kan titin Zariya a Kano

Gwamnati ta rufe katafaren shagon Sahad stores a Abuja

Kungiyar ma su motocin sufuri ta kasa RTEAN ta dakatar da shugaban tashar kwanar Dawaki

Alkalin Kotun Mai shari’a Simon Amobeda a hukuncin da ya yanke a ranar Juma’a ya yi watsi da karar da kungiyar masu hada-hadar magunguna ta Najeriya, da wasu mutane shida suka shiga saboda rashin cancanta.

Shugabancin kungiyar yan maganin na jahar Kano, sun ce za su magantu kan batun.

 

Globaltracker

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *