Wata Kungiya Ta Bukaci Sarki Aminu Ado Ya Bar Kano Don Wanzar Da Zaman Lafiya

Spread the love

Kungiyar Arewa Social Contract Initiative ta yi kira ga Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero da ya bar jihar domin wanzar da zaman lafiya a jihar.

Shugaban kungiyar na kasa, Kwamared Sani M. Darma ne ya yi wannan kira a ranar Lahadi a wani taron manema labarai a Kano.

Darma ya bayyana cewa dawowar Aminu Bayero Kano da yunkurin kwato masa mukaminsa zai iya haifar da tashin hankali, rudani da rikici a jihar.

Ya kuma kara da cewa ko da Aminu Ado Bayero na son ya karbi karagar mulkin kano, da sai ya ci gaba da zama a wata jiha kuma ya bi tsarin da ya dace.

“Abin takaici ne a ce bayan sauke Alhaji Aminu Ado Bayero daga karagar mulki, ya amince da tsige shi, ya kuma mika dukkanin kayan sarauta , amma wasu daga gwamantin tarrayya suka zuga shi ya dawo Kano domin a mayar masa da mukaminsa”. Inji Darma.

Kadaaura24

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *