Wata mata ta haihu a tashar mota a Najeriya

Spread the love

Hukumar agajin gaggawa ta sanar cewa matar da ba a bayyana sunanta ba tana jiran shiga motar bas ne a tashar Onipanu Bus Stop a lokacin da ba zato ba tsammani ta shiga naƙuda a ranar Litinin.

Mata ƴan kasuwa ne suka taimaka ma ta, yayin da masu ba da agajin gaggawa suka garzaya wurin.

Hukumar agajin gaggawa ta ƙara da cewa, ta haifi ɗa namiji, kuma tuni aka kai mahaifiyar da yaron asibiti. domin duba lafiyarsu

Babu wani ƙarin bayani da aka bayar game da su baya ga haka, amma ‘yan Najeriya a shafukan sada zumunta na ta wallafa sakonnin taya murna har ma da shawaran sunayen da za a raɗawa jaririn.

Gamayyar hukumomin tsaro a Kano sun tattauna da shugabancin jam’iyun siyasa gabanin zaben cike gibi da za a sake yi a Kunchi/Tsanyawa.

Hukumar kwastam ta Najeriya za ta raba kayan abincin da aka kama a faɗin ƙasar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *