Wutar Lantarki Ta Kashe Barawon Taransufoma

Spread the love

Wutar lantarki ta kashe wani barawon tiransufoma a unguwar Jattu da ke Karamar Hukumar Etsako ta yamma a Jihar Edo.

Al’ummar unguwar dai sun wayi gari ne da ganin gawar barawon da ake zargi, tana lilo a jikin turakun wutar lantarki da ke hada da tiransfomar.

Sai da wanda ake zargin ya yanke wayoyin da ka karkashin tiransufomar, ya ajiye su a gefe, sannan ya hau sama zai yanko dogayen wayoyin da ke raba wutar, inda a nan ne ya gamu da ajalinsa.

Kotun Koli Ta Tabbatar Da Fintiri A Matsayin Gwamnan Adamawa

Sojoji sun kuɓutar da mutum uku da akayi garkuwa da su a jihar Taraba

Shaidu sun bayyana cewa daga bisani jami’an Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Edo (BEDC) sun zo sun dauke gawar suka tafi da ita.

Kakakin ’yan sandan jihar, SP Chidi Nwabuzor, dai ya ce ba shi da labarin abin da ya faru.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *