Yadda Ake Zargin Mai Tallan Kifi Da Sayar Da Zinaren Sata N60m A Abuja.

Spread the love
Abuja

Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, Abuja ta kama wasu mutum uku da ake zargi da fasa wani gida tare da sace zinare da wasu kayayyaki masu tsada a Abuja.

Mataimakin Kwamishinan ’Yan sanda, ACP Olumuyiwa Adejobi ne, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja.
An kama mutanen ne bayan wani bincike da tawagar Binciken Bayanan Sirri (IRT) ta gudanar, wanda ya gano wadanda ke da hannu a laifin.

Bincike ya nuna cewa  wanda ake zargi na farko yana sana’ar sayar da kifi a Kasuwar Kifi ta Kado da ke Abuja.

Sanarwar ta ce “waɗanda ake zargin sun yi wa gidaje uku fashi a unguwar Lugbe, kafin su shiga na huɗu sun yi amfani da wani ƙarfe wajen banƙara tagar gidan inda ta nan suka samu damar shiga gidan.

“Suna shiga gidan, kai-tsaye suka shiga binciken abin da za su uya sacewa.

“A lokacin da suke lalube, sai suka hangi wani akwati a ajiye, nan take suka ɗauka suka tafi da shi.

“Sun yi amfani da guduma wajen buɗe akwatin, inda suka samu kuɗi, takardu, da zinare a ciki.

Sai dai na farko da ake zargin, ya kira mai saye sannan ya sayar da kayan satar, kan kuɗi Naira miliyan 60,” a cewar sanarwar.

Rundunar ta ce da zarar ta kammala bincike za ta miƙa su zuwa kotu domim girbar abin da suka aikta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *