Fadar Shugaban Ƙasa, ta musanta raɗe-raɗin cewar Shugaba Tinubu na fifita yankin Kudu Maso Yamma a kan sauran yankuna wajen rabon muƙaman da suka shafi sha’anin tsaro.
Wannan na zuwa ne, biyo bayan naɗa Manjo Janar Olufemi Oluyede, a matsayin Muƙaddashin Babban Hafsan Sojojin Ƙasan Najeriya, inda a kafafen sada zumunta aka zargi Tinubu da fifita ƙabilar Yarbawa.
An naɗa Oluyede ne, don ya maye gurbin Janar Tahoreed Lagbaja, Babban Hafsan Sojojin Kasa, wanda ya fita ƙasar waje domin neman lafiya.
Wasu ’yan Najeriya sun nuna cewar akwai manyan janar-janar masu ƙwarewa da za a iya bai wa wannan muƙami maimakon ɗauko wani daga yankin Kudu Maso Yamma.
Sai dai Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Sunday Dare, ya musanta raɗe-raɗin ta hanyar wallafa jerin sunayen shugabannin hukumomin tsaro da Tinubu ya naɗa.
AMINIYA
- Sojojin Najeriya sun kama wani ƙasurgumin ɗanbindiga da suke nema ruwa a jallo
- Amnesty ta nemi Shugaba Tinubu ya saki duk masu zanga-zangar tsadar rayuwa