‘Yan Najeriya sun bai wa jami’an gwamnati cin-hancin naira biliyan 721 a 2023 – NBS

Spread the love

Wani rahoton bincike da hukumar ƙididdiga ta Najeriya (NBS) ta fitar ya bayyana cewa ‘yan Najeriya sun bai wa jami’an gwamnatin ƙasar naira biliyan 721 (dala biliyan 1.26) a matsayin cin-hanci a 2023.

Rahoton ya ce ‘yan Najeriyar sun ba da cin-hancin ko kuma rashawa sau miliyan 87, amma adadin ragi ne idan aka kwatanta da miliyan 117 da suka bayar a 2019.

Cikin duka ‘yan Najeriyan da suka ga aƙalla wani jami’in gwamnati ɗaya cikin wata 12 kafin gudanar da binciken a 2023, kashi 27 sun bai wa jami’in hanci.

Idan aka kwatanta da abin da aka saba gani a baya, hakan na nufin yawan biyan rashawa a Najeriya ya ragu kaɗan zuwa kashi 23 tun daga 2019, lokacin da aka samu kashi 29 da suka ba da hanci.

A wuraren da kuma aka tambayi cin-hanci amma mutane suka ƙi bayarwa, an ba da cin-hancin fiye da sau ɗaya cikin haɗuwa uku (kashi 34 cikin 100) a 2023.

Sai dai kuma kashi 70 cikin 100 na mutanen da aka nemi su ba da rashawar a 2023 sun ƙi bayarwa sama da sau ɗaya.

Kazalika, binciken ya gano cewa raguwar ba da rashawar ta fi yawa a yankin arewa maso yammacin Najeriya da kashi 76, duk da cewa sauran yankunan sun samu sama da kashi 60 cikin 100.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *