’Yan Sanda 20 Aka Ji Wa Rauni A Zanga-zangar Gombe’

Spread the love

Kwamishinan ’Yan Sandan Gombe, Hayatu Usman, ya bayyana cewa an jikkata jami’ansa 20 a lokacin zanga-zangar tsadar rayuwa da aka gudanar a jihar.

Ya ce an yi arangama sosai inda aka samu asarar dukiyoyin gwamnati da na al’umma, amma da taimakon sauran hukumomin jami’an tsaro an shawo kan lamarin tare da dawo da zaman lafiya a jihar.

Kwamishinan ya bayyana cewa duk da haka bai samu rahoton rasa rai ko daya ba sakamakon zanga-zangar.

Amma ya ce zaman lafiya ya dawo a jihar, al’umma sun ci gaba da hada-hadarsu, ’yan kasuwa sun bude shagunansu, sannan jami’an tsaro suna ci gaba da sintiri da kula da abin da ka iya je ya dawo.

Da yake jawabi bayan kammala zaman majalisar tsaron jihar a ranar Litinin, Hayatu Usman ya bayyana cewa an kwantar da jami’an ne a asibitin gidan gwamnatin jihar.

Ya kuma yaba wa al’ummar gari musamman wasu iyayen kirki da suka taimaka musu wajen dawo da kayayyakin da wasu daga cikin ’ya’yansu suka sace a lokacin zanga-zangar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *