Yan Sanda Sun Gurfanar Da matar Da Ake zargin Ta Yanke Maƙarfafar Mijin Ta A Kano

Spread the love

Kotun majistret mai lamba 54 ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Ibrahim Mansur Yola a jihar Kano, ta fara sauraron wata ƙara wadda ƴan sanda suka gurfanar da wata mata mai suna Maryam Imam mazauniyar garin Tofa, inda ake zargin ta da laifin yanke makarfafar mijinta Abubakar Imam.

Yayin da aka karanta wa matar ƙunshin tuhumar da ake mata ta amsa nan ta ke, ta kuma shaida wa Alkalin kotun cewar tun farko auren dole aka yi mata, kuma shi mai gidan na ta duk da yasan cewar bata kaunarsa amma kullum sai ya ɓata mata rai.

Mai Shari’a Mansur Yola ya ayyana cewar za a yi hukunci ranar 11/6/2024 dan gudun na ma ya dahu romo ɗanye, tunda dai ance Abubakar din yana kwance a asibiti ya na ci gaba da samun kulawar likitoci.

Kotun ta kuma umarci a ajiye matar a gidan gyaran hali zuwa waccan ranar da aka sanye domin yanke hukuncin.

Dala FM ta so zantawa da matar da ake zargi da yankewa mijin nata maƙarfafa, sai dai dogarawan gidan gyaran hali sun shiga tsakani, hakan ya sa lamarin ya gagara.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *