Yan sanda sun kashe mutum 1, sun kama masu laifi 6 a Kaduna

Spread the love

 

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta samu nasarar dakile ayyukan masu garkuwa da mutane tare da kashe mutum ɗaya daga cikinsu.

Haka kuma, sun kama wasu mutane shida da ake zargi da aikata laifuka daban-daban.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

A cewarsa, sun kama mutum uku da ake zargi da aikata fashi da makami, tare da wasu uku da ake zargi da safarar bindigogi.

An kuma samu kayayyaki kamar bindigogi guda biyu, bindiga ƙirar gida guda ɗaya da kuma harsasai 216.

 

ASP Mansur, ya ce a ranar 8 ga watan Disamba, jami’an ’yan sanda daga ofishin yanki Kasuwar Mata a Sabon Gari sun kai farmaki wani gidan karuwai da ke Titin Nupe bayan samun rahoton sirri.

A waje , sun kama wani Adamu Yahaya mai shekara 35 tare da bindiga ƙirar gida, kwanson harsasai, da sarƙa.

Har ila yau, a ranar 8 ga watan Disamba, jami’an ‘yan sanda na Barnawa sun kama wasu mutum biyu; Andrew Emmanuel da Mendwas Peter Bulus.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *