Kwamishinan ‘yan sandan birnin tarayya Abuja, Benneth Igweh, ya bayar da umarnin gudanar da binciken kisan da wasu da ake zargi ‘yan fashi suka yi wa wani tsohon Janar a gidansa da ke Abuja.
Maharan sun kutsa gidan marigayin – Burgediya Janar Uwem Udokwere mai ritaya – inda suka kashe shi.
Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan birnin tarayyar, ASP Josephine Adeh ta fitar, ta ce an kashe tsohon janar ɗin a gidansa da ke rukunin gidajen Sunshine a unguwar Lokogoma da ke birnin tarayyar, ranar Asabar da tsakar dare.
Kwamishinan ‘yan sandan ya kuma jajanta wa iyalan marigayin, tare da alƙawarta farauto waɗanda suka yi aika-aikar domin gurfanar da su a gaban shari’a.
”Za mu yi duk abin da ya kamata don tabbatar da kamo maharan domin gurfanar da su a gaban shari’a domin su girbi abin da suka shuka”, in ji sanarwar.