Rundunar yan sandan jahar Kano, ta samu nasarar kama wani matashi, mai suna Abba Garba wanda akafi sani da ( Kuda) bisa zarginsa da hallaka Zaharaddin Iliyasu, ta hanyar yanka wuyansa wukar Zarto sakamakon sun samu sabani da marigayin.
Kakaki rundunar yan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya aike wa da jaridar idongari.ng, da yammacin ranar Asabar.
Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne a yankin Sabontitin Phanshekara karamar hukumar Kumbotso dake jahar, tun a daren ranar Juma’a 29-3-2024.
- Idongari.ng Facebook Latsa domin Samun labarai Da Dumi-dumin su
- EFCC ta kama mutum 74 da ake zargi da aikata zamba ta intanet a Ogun
SP Kiyawa, ya ce jami’an yan sandan Panshekare ne suka samu nasarar cafke matashin, a lokacin da yake kokarin guduwa jamhuriyar Nijar .
Yanzu haka dai ya na tsare a hannun yan sandan domin ci gaba da amsa tambayoyi kafin a gurfanar dashi a gaban kotu.
- Ana Zargin Wani Dan Kasar Chaina Da Yi Wa Yar Direbansa Ciki A Kano.
- CBN na neman mutanen da suka ci bashinsa fiye da naira biliyan 260